KARSHEN LUWADI MUGUN
ABOKI MABUDIN WAHALA
PART 5
@na Faisal Ahmad
07050222260
Bamu jima muna tafiya ba sai gamu a Beirut kasuwar yan wayo
yi muka shiga wani shago da
shigar mu idona ya fara
hangomin wayoyin zamani Sai jinai
dauda ya cemin "wacce ya
kamata ka zaba" nace duk wanda ka daukar min tayi
Sai gani nai ya dau ko wata waya
kirar blackberry Z30 aka fada
mana kudin ta dauda ya kirgo kudi
ya biya muka futo muka
hau mashin sai gamu a kofar wani babban
hotal Nan naji gabana yai
mugun faduwa !!!
Saboda ban taba zuwa hotal ba sai
dai labarin nake ji a wajan
su prince shima labarin sai in sun dawo daga gidan rawa.
Su kansu inaji suna cewa wannan
hotal din Bakaranin mai kudi
bane ya ke iya kamawa amma sai
gashi yau nine zan shiga
cikin sa, Nayi mamakin yanda muka shiga
cikin hotal din ba wani
Wanda ya tambaye mu har muka
isa bakin wata kofa mai
number 0041 sai gani nai dauda ya
curo wani card mai kama da ATM ya zura shi acikin kofar da
kin sai gani nai kofar ta na
budewa
Kai gaskiya abin ya ban mamaki
abinda muke gani acikin film
din turawa amma yau sai gashi ina gani,
Shigarmu ke da wuya kai na ya
juye naga kamar awata
sabuwar duniya muke kai wannan
dakin ko gidan manyan
masu kudi sai an bin cika. Muka samu guri muka zauna
abakin gado,
Na tambayi dauda nace wannan
hotal din nawa ake biya duk
kwana daya dauda yace"wannan
dakin yakai ki manin naira dubu arba,in da biyar 45000" cikin
tambaya nace dauda wai
yanzu mutum ne yake biyan
wannan kudin Ko kuma?? Dauda
yayi dariya sai jinai yace "tsaya in
tashi inje in watsa ruwa saboda yau mai gida zai dawo"
yatashi ya shiga wani irin ban
daki mai kama da gidan glass ya
shiga ya watsa ruwa ya fito
daga shi sai wata yar karamar
Riga ya cemin "shaheed ya kamata kai ma kashiga kadan
watsa ruwa sabo da yau anyi
rana " natashi na shiga nima na
dan watsa ruwa na fito ya
dauko wani turare mai kamshi ya
feshe duka cikin dakin Minti kadan dakin ya dau wani rin
kamshi
Kai amma wanna turaran ya shigar
min har tsakiyar kaina ban
taba jin irin wannan turarenba
dauda ya bude wata durowa irin ta jikin bango ya dauko wani man
shafawa ya cemin"wannan
maganin ciwon baya ne" ya cire
rigar sa ya kwanta akan gado
yace in shafa masa nakarba na
bude robar na lakato na fara sha fa masa sai jinai yana wani irin
nishi kasa.kasa yace in bar
shi haka yatashi zaune yace
"shaheed kai ma kana so in shafa
maka"cikin sauri nace a,a saboda
ni bana ciwon baya sai naga yana dariya akaro na biyu yace "
tsaya in tashi in dafamana
shayi nasan kai ma abocin shan
shayi ne "
Ya tashi ya dafamana shayi a
cupy herta ya dauko wani irin ganyan shayi wanda bantaba
ganin irin saba,
Amma banyi mamaki ba tunda ba,a
Gida muke ba muna cikin
Wata sabuwar daula ce minti
kadan sai gashi da kofuna guda biyu a hannun sa ya mikomin daya
ina karba naji wani irin
kamshi ya daki hanci na ya zauna
muna sha muna hira nace
kai !! amma wannan shayin yayi
dadi so sai dauda yace "ai dole in karrama ka a wannan ranar
minti kadan sai jinai han
kalina ya fara gushewa can sai
jinai ina limshe ido jiki na
bakwari ina magana a hankali naga
dauda yana matsowa kusa dani.....
Wednesday, May 15, 2019
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
ads1
Author Details
new platform in northern arewa

No comments:
Post a Comment